Skip to main content

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Yankuna 225 A Kano Da Jigawa



 By:- mujahid Muhammad tijjani


Ambaliyar ruwa ta lalata yankuna 225 a kananan hukumomi 31 dake kano da jigawa a cewar hukumar bayar da again gaggawa ( NEMA)


Babban jami'in NEMA mai kula da kano da

 jigawa, Dr.Nuradden Abdullahi ya sanar da

 hakan yayin zantawa da manema labarai a

 ranar Sanar.


A cewarsa ambaliyar nada nasaba ne da

 ruwan Sama na mako da ake tafkawa tun

 daga watan yuli zuwa yanzu.


Yace wannan yanayi Wanda ba yanzu aka

 soma fuskantar Saba, ya tilasrawa mutane

 da dana rasa matsuguni da sasu yin hijira 

 zuwa wasu yankuna na Arewacin kasar.


Kananan hukumomin da ambaliyar ruwan

 ta shafa a kano sun hada da Tudun Wada,

 Doguwa, Kibiya, Kiru, Gwale, Danbatta,

 Bagwai, Ajingi, Albasu, Shanono , Tsanyawa,

 Rimin Gado, da Dawakin Kudu.


A jihar jigawa kuma akwai kananan

 hukumomi irinsu, Kafin Hausa, Malam

 Madori, Hadeja, Guri, Auyo, Birniwa, Jahun,

 Miga, Kiyawa,  Birnin Kudu, Babura,

 Gwaram, Kaugama, Dutse, da Kirikasamma.


Abdullahi ya ce ambaliyar ta lalata gidaje da

 gine-gine da gonaki  da sauran tarin

 dukiyoyi .


A kwanakin baya ne aka yi ruwan Sama

 kamar da bakin kwarya da ya lalata

 yankuna da dama a jihohin kano da jigawa,

 Wanda yayi sanadin asarar rayuka da

 dukiyoyi na miliyoyin naira.


Aminiya ta rawaito cewa, ambaliyar ruwan

 na zuwa ne a yayin da NEMA ke cigaba da

 gargadin masu ruwa da tsaki da su dauki

 matakan dasuka dace domin kaucewa

 ambaliyar ruwan dake addabar al'umma

 daban-daban a halin yanzu.


A farkon wannan watan ne Hukumar

 hasashen yanayi (NiMet) ta Sanar da cewa

 ana sa ran saukar ruwan Sama kusan duk

 Rana a jihohin arewa 19 ciki harda kano da

 jigawa a tsakanin Agusta zuwa satumba

 shekara ta 2022.


Comments