Skip to main content

Yadda mai babur ya kashe mutane 13 a wajen buki a calabar

 


Hadarin ya afkune a lokacin wani buki a Calabar babban birnin jihar Cross River dake Kudu maso kudancin Nigeria, lamarin da ya janyo mutuwar mutum 13 tare da raunata mutum 24.

Mai magana da yawun rundunar 'Yan Sandan jihar, SP Irene Ugbo, ya sanar da BBC cewar suna cigaba da yunkurin ceto rayukan wadanda abun ya rutsa dasu.

Hadarin dai ya afku ne a ranar Talata a lokacin bikin wasa da Babura da aka gabatar a titin Mery slessor a bogobiri, daya daga cikin manyan hanyoyin da aka tanada domin wasan na  bana.

Wani ganau ba jiyau ba yace babur din ya kwacewa matukin dake gudun wuce sa'a, wanda hakan ya sa  ya kutsa cikin 'yan kallo.

SP  Ugbo, ya ce "wadanda ake zargi na hannunsu bayan faruwar lamarin".

Gwamnan jihar Cross River Farfesa Ben Ayade, ya soke bukin, inda ya bukaci a gaggauta yin binkice kan faruwar al'amarin.

A wata sanarwa da daraktar yada labarai ta jihar, Cristiana Ita, ta ce "gwamnan jihar nason sanin yadda matukin babur din ya samu damar kutsawa inda ake bukin, dukda an rufe hanyar ga mutanen gari.

SP Ugbo, ya ce 'yan sanda sun maido da zaman lafiya bayan faruwar lamarin.

A wasu hotunan bidiyo masu tayar da hankali da ke yawo a kafafen sada zumunta, sun nuna munanan raunukan da wayanda hadarin ya ritsa dasu  suka samu.

Bukin hawa babura na daya daga cikin manyan wasanni  kalakuwa da akeyi a birnin na Calabar, a jihar wanda tayi fuce wurin wajen shirya irin wayennan bukukuwan.

Gwamnatin jihar ta Cross River ce dai ta dauki nauyin bukin, da ake gudanar wa shekara-shekara, wanda hakan yasa yazama daya daga cikin  bukukuwan da yake janyo hankala a Nigeria a karshen ko wacce shekara. 

An fara gudanar da bikin dai a shekarar 2004 a matsayin wasan janyo hankulan masu yawon bude ido  a birnin Calabar.

A yayin bukin mutuka babura kan gudanar da nau'ukan wasanni da babur iri-iri, domin kayatar da masu kallo.

 A duk lokacin da ake gudanar da bikin, akan takaita zurga zurgan ababen hawa a hanyoyin da aka  shirya cewa masu wasa da baburan zasu bi.


Comments

Popular posts from this blog

NECO Result 2022/23 Is Out: Check It Now

  National Examination Council {NECO}  2022/23 result is out. Candidates that participated in the SSCE internal can now check their results online. You will however need to purchase the results checking token to be able to access your result online. The NECO June/July Examination is the examination taken by Students in their last stage of secondary school education. How to check NECO Result for 2022/23 Step 1. Getting a NECO scratch card. The first step to successfully check your NECO Result is to get a Valid NECO scratch  card, after buying the scratch card gently scratch and remove the materials covering the pin. Note that :The pin and the serial number are the most important part of the NECO scratch card. Step 2: visit the NECO June/July result website. The next step after buying the scratch card is to visit the portal where the results can be accessed. To visit the website click on the link below  https://result.neco.gov.ng/ Step 3: choosing the right exam type T...

NPC Training Updates on SMS/Email Invitations

  It is no news that the National Population Commissions NPC has begun to send training invitations to the applicant of the NPC recruitment for the conduct of 2023 housing and population census. Therfore if your application status was 'approved', in the situation on the ground now, it's must likely you won't receive any SMS/Email from must LGAs. Kindly go to your LGAs on Monday 10th April, 2023. To confirm your name, venue and  class on the list. Training starts on the 11th - 17th of April. After the training, items to be given to you include:   ・Tab   ・Power bank    ・Reflector jacket    ・T-shirt    ・Wait bag    ・Cup Good luck....     

Tarihi 5 da Ronaldo ya kafa A wasan Portugal da Liechtenstein

Tarihi 5 da Ronaldo ya kafa A wasan Portugal da Liechtenstein.  Ina masoyan dan wasa Cristiano Ronaldo ku karanta dan sani ga garumar rawar da gwanin naku ya taka...   Ronaldo ya jefa kwallo ta 60 a bugun tazara a tarihi. By : Mujahid Muhammad Tijjani  24/03/2023 : 2:56pm Cristiano Ronaldo ya bugawa kasarsa ta Portugal wasa na 197, ya kuma ci kwallo biyu a wasan neman shiga Euro 2024, bayan doke Liechtenstein da ci 4 da nema.  Dan wasan mai shekaru 38, shine kan gaba a yawan jefa kwallaye  a tawagar a harihi kusan shekara 120 kawo yanzu.  Dan wasan ya fara bugawa kasarsa kwallo ne tun a shekarar 2003, wanda a gasar kofin duniya na 2022 wanda aka buga a Qatar, ya zama na farko da ya zura kwallo a ko wacce gasa a kofin duniya.  Minti takwas da fara wasa Portugal taci kwallo ta hannun Joao cancelo, Minti biyu da komawa zagaye na biyu dan wasa Bernardo silver ya kara ta biyu.  Sai Cristiano Ronaldo ya ci ta ukku a bugun fenariti, sannan ya kara t...