Skip to main content

Kotu Tasa Murja Kunya Da Abokan Ta Sharar Asibiti Da Masallaci

 Murja zatayi sharar Asibiti, abokanta kuma zasu rika share masallaci.




Kotun shari'ar musulunci dake Zaman ta a filin Hokey ta yankewa jarumar nan ta Tiktok wato Murja Ibrahim Kunya da abokanta hukuncin sharar masallaci da kuma asibiti.

Abokan Murja maza, wadanda aka gurfanar dasu tare da ita, Ashiru Idris Mai wushirya, Aminu BBC da kuma Sadik Shehu Shariff zasu dunga sharar masallacin Murtala da ke Kano, da bandakunan sa na tsahon mako uku.

Ita kuma Murja zata dunga share asibitin Murtala, ta rika zuwa tana yin awa 8 kullum. a ofishin hisba, kuma ta goge wasu bidiyoyin ta a shafukan sada zumunta, sannan an haramta mata gudanar da taron jama'a.

Kotu ta yanke musu hukuncin ne a shari'ar da aka gurfanar dasu kan zargin Yada batsa a kafar Tiktok da kuma bata tarbiya, zargin da suka musanta.

Gabanin zaman Kotun na ranar Alhamis, saida Alkali, Mai shari'a Abdullahi Halliru, ya turasu zaman wakafi zuwa gidan yari akan zargin.

A zaman na ranar Alhamis, mai gabatar da kara, lauyan gwamnatin jahar Kano, Barista  Lamido Abba Soron Dinki, ya roki Kotun da'a sake karantawa Murja takardar tuhumar da ake mata nayin batsa, ta yar da hankali da barazanar Zaman lafiya a cikin Al'umma, wanda hakan ya sabawa sashi na 355 da kuma na 33 dana 275 na kundin shari'ar musulunci.

Sannan ya gabatarwa da Kotun takardar yarjejeniya ta sulhu wacce Murja ta rubuta kan cewa ta amsa laifin ta, ta hannun lauyan ta Barista A E Saka.

Daga nan ne mai shari'a, Abdullahi Halliru yayi umarnin da a karanta mata takardar hukuncinsa.

Takardar ta kunshi cewa dole ne ita wacce ake tuhuma ta goge dukkan wani bidiyo ko sauti data wallafa mai dauke da batsa data wallafa a shafinta na sada zumunta.

An kuma haramta wa Murja shirya duk wani nau'in taro na jama'a da zai Iya jawo batanci ko bata tarbiya ko tayar da tarzoma ko kuma tada hankulan jama'a.

Sai kuma sharadin zuwa ofishin  hukumar hisba a duk ranar Alhamis da Litinin daga karfe 12 na rana zuwa 5 na yamma har na tsahon wata shida.

Haka kuma zata ringa gabatar da kanta a kotu duk bayan wata daya tare da ma'aikacin hukumar hisba.

Takardar Kotun tace sabawa wadannan sharadun zai iya janyowa a kara mata lokaci akan wanda Kotun ta Sanya mata na wata shida.

Bayan karanta mata ne mai shari'a ya tambaye ta ko ta gamsu, nan take ta amsa da cewa ta gamsu.

Idan za'a Iya tunawa, majissar malamai ce ta jahar Kano takai karar Murja Ibrahim Kunya ga yan'sanda inda su kuma suka gurfanar da ita a gaban kotu.

Ana tuhumar Murja da laifin  hada kai da Sunusi Oscar 442 da Safara'u da Dan Maraya da Amude Booth da Samha M Inuwa da Ummi Shakira, wanda yanzu haka suka cika wandon su da iska, inda suke bin wata Waka ta Ado Gwanja da Kawo Dan Sarki inda suke Yada shi a shafukan sada zumunta wanda hakan zai iya bata tarbiyan Al'ummar jihar Kano.


Comments

Popular posts from this blog

NECO Result 2022/23 Is Out: Check It Now

  National Examination Council {NECO}  2022/23 result is out. Candidates that participated in the SSCE internal can now check their results online. You will however need to purchase the results checking token to be able to access your result online. The NECO June/July Examination is the examination taken by Students in their last stage of secondary school education. How to check NECO Result for 2022/23 Step 1. Getting a NECO scratch card. The first step to successfully check your NECO Result is to get a Valid NECO scratch  card, after buying the scratch card gently scratch and remove the materials covering the pin. Note that :The pin and the serial number are the most important part of the NECO scratch card. Step 2: visit the NECO June/July result website. The next step after buying the scratch card is to visit the portal where the results can be accessed. To visit the website click on the link below  https://result.neco.gov.ng/ Step 3: choosing the right exam type T...

NPC Training Updates on SMS/Email Invitations

  It is no news that the National Population Commissions NPC has begun to send training invitations to the applicant of the NPC recruitment for the conduct of 2023 housing and population census. Therfore if your application status was 'approved', in the situation on the ground now, it's must likely you won't receive any SMS/Email from must LGAs. Kindly go to your LGAs on Monday 10th April, 2023. To confirm your name, venue and  class on the list. Training starts on the 11th - 17th of April. After the training, items to be given to you include:   ・Tab   ・Power bank    ・Reflector jacket    ・T-shirt    ・Wait bag    ・Cup Good luck....     

Tarihi 5 da Ronaldo ya kafa A wasan Portugal da Liechtenstein

Tarihi 5 da Ronaldo ya kafa A wasan Portugal da Liechtenstein.  Ina masoyan dan wasa Cristiano Ronaldo ku karanta dan sani ga garumar rawar da gwanin naku ya taka...   Ronaldo ya jefa kwallo ta 60 a bugun tazara a tarihi. By : Mujahid Muhammad Tijjani  24/03/2023 : 2:56pm Cristiano Ronaldo ya bugawa kasarsa ta Portugal wasa na 197, ya kuma ci kwallo biyu a wasan neman shiga Euro 2024, bayan doke Liechtenstein da ci 4 da nema.  Dan wasan mai shekaru 38, shine kan gaba a yawan jefa kwallaye  a tawagar a harihi kusan shekara 120 kawo yanzu.  Dan wasan ya fara bugawa kasarsa kwallo ne tun a shekarar 2003, wanda a gasar kofin duniya na 2022 wanda aka buga a Qatar, ya zama na farko da ya zura kwallo a ko wacce gasa a kofin duniya.  Minti takwas da fara wasa Portugal taci kwallo ta hannun Joao cancelo, Minti biyu da komawa zagaye na biyu dan wasa Bernardo silver ya kara ta biyu.  Sai Cristiano Ronaldo ya ci ta ukku a bugun fenariti, sannan ya kara t...