Skip to main content

Kotu Tasa Murja Kunya Da Abokan Ta Sharar Asibiti Da Masallaci

 Murja zatayi sharar Asibiti, abokanta kuma zasu rika share masallaci.




Kotun shari'ar musulunci dake Zaman ta a filin Hokey ta yankewa jarumar nan ta Tiktok wato Murja Ibrahim Kunya da abokanta hukuncin sharar masallaci da kuma asibiti.

Abokan Murja maza, wadanda aka gurfanar dasu tare da ita, Ashiru Idris Mai wushirya, Aminu BBC da kuma Sadik Shehu Shariff zasu dunga sharar masallacin Murtala da ke Kano, da bandakunan sa na tsahon mako uku.

Ita kuma Murja zata dunga share asibitin Murtala, ta rika zuwa tana yin awa 8 kullum. a ofishin hisba, kuma ta goge wasu bidiyoyin ta a shafukan sada zumunta, sannan an haramta mata gudanar da taron jama'a.

Kotu ta yanke musu hukuncin ne a shari'ar da aka gurfanar dasu kan zargin Yada batsa a kafar Tiktok da kuma bata tarbiya, zargin da suka musanta.

Gabanin zaman Kotun na ranar Alhamis, saida Alkali, Mai shari'a Abdullahi Halliru, ya turasu zaman wakafi zuwa gidan yari akan zargin.

A zaman na ranar Alhamis, mai gabatar da kara, lauyan gwamnatin jahar Kano, Barista  Lamido Abba Soron Dinki, ya roki Kotun da'a sake karantawa Murja takardar tuhumar da ake mata nayin batsa, ta yar da hankali da barazanar Zaman lafiya a cikin Al'umma, wanda hakan ya sabawa sashi na 355 da kuma na 33 dana 275 na kundin shari'ar musulunci.

Sannan ya gabatarwa da Kotun takardar yarjejeniya ta sulhu wacce Murja ta rubuta kan cewa ta amsa laifin ta, ta hannun lauyan ta Barista A E Saka.

Daga nan ne mai shari'a, Abdullahi Halliru yayi umarnin da a karanta mata takardar hukuncinsa.

Takardar ta kunshi cewa dole ne ita wacce ake tuhuma ta goge dukkan wani bidiyo ko sauti data wallafa mai dauke da batsa data wallafa a shafinta na sada zumunta.

An kuma haramta wa Murja shirya duk wani nau'in taro na jama'a da zai Iya jawo batanci ko bata tarbiya ko tayar da tarzoma ko kuma tada hankulan jama'a.

Sai kuma sharadin zuwa ofishin  hukumar hisba a duk ranar Alhamis da Litinin daga karfe 12 na rana zuwa 5 na yamma har na tsahon wata shida.

Haka kuma zata ringa gabatar da kanta a kotu duk bayan wata daya tare da ma'aikacin hukumar hisba.

Takardar Kotun tace sabawa wadannan sharadun zai iya janyowa a kara mata lokaci akan wanda Kotun ta Sanya mata na wata shida.

Bayan karanta mata ne mai shari'a ya tambaye ta ko ta gamsu, nan take ta amsa da cewa ta gamsu.

Idan za'a Iya tunawa, majissar malamai ce ta jahar Kano takai karar Murja Ibrahim Kunya ga yan'sanda inda su kuma suka gurfanar da ita a gaban kotu.

Ana tuhumar Murja da laifin  hada kai da Sunusi Oscar 442 da Safara'u da Dan Maraya da Amude Booth da Samha M Inuwa da Ummi Shakira, wanda yanzu haka suka cika wandon su da iska, inda suke bin wata Waka ta Ado Gwanja da Kawo Dan Sarki inda suke Yada shi a shafukan sada zumunta wanda hakan zai iya bata tarbiyan Al'ummar jihar Kano.


Comments

Popular posts from this blog

NECO Result 2022/23 Is Out: Check It Now

  National Examination Council {NECO}  2022/23 result is out. Candidates that participated in the SSCE internal can now check their results online. You will however need to purchase the results checking token to be able to access your result online. The NECO June/July Examination is the examination taken by Students in their last stage of secondary school education. How to check NECO Result for 2022/23 Step 1. Getting a NECO scratch card. The first step to successfully check your NECO Result is to get a Valid NECO scratch  card, after buying the scratch card gently scratch and remove the materials covering the pin. Note that :The pin and the serial number are the most important part of the NECO scratch card. Step 2: visit the NECO June/July result website. The next step after buying the scratch card is to visit the portal where the results can be accessed. To visit the website click on the link below  https://result.neco.gov.ng/ Step 3: choosing the right exam type The NECO exam type y

BUK Release 2022/2023 Admission list on JAMB CAPS

  Bayero University kano, has released admission list for the 2022/2023 academic season on JAMB CAPS.  This is to inform all candidates who took part in the 2022 /2023 Admission screening exercises that they can now proceed to check if their names are on the provisional admission list of successful candidates uploaded on JAMB CAPS.  Candidates are to follow the procedures below to check: 1. Visit: https://www.jamb.gov.ng/Efacility and login with your registered email address and password to access your dashboard  2. click on "check admission status"  3. Click on "Access my CAPS"  4. Click on "Admission status" to see if you have been offered admission.  Candidates who have been offered admission are to proceed to click "Accept" or Reject" to indicate acceptance or rejection of the admission offer.  Congratulations to the admitted candidate.  NB: Admission is a gradual process, not yet admitted candidates are advised to stay glued to their po

Sabuwar wakar Lsvee tare da Hamisu breaker dorayi

  Ga dan Karmin video din wakar da Mawaki lsvee da Hamisu breaker dorayi zasu saki wata Waka mai suna Ole Zasu saki wakar  ranar laraba 31/8/2022 da misalin karfe 11 ga kadan daga cikin video din wakar Kuci gaba da bibiyar domin samin wakar cikin sauki hardama wasu sabbin wakilin.